• About
  • Contact Us
  • DMCA/Disclaimer
  • Privacy Policy
  • Sample Page
BestArewaMusic
No Result
View All Result
No Result
View All Result
BestArewaMusic
No Result
View All Result
  • Music
  • Videos
  • Hausa HipHop Music
  • News
  • International NEWS
  • Sports
Home News

Dalilan Sauken Sarkin Kano Muhammad Sunusi Na Biyu

AB Gentle by AB Gentle
March 9, 2020
in News
Reading Time: 7 mins read
0
42
SHARES
220
VIEWS
Share on FacebookShare on Twitter

Rashin Biyayya

Sarkin Kano yana nuna rashin biyayya ga umarnin ofishin gwamna da na sauran hukumomin gwamnati, ciki har da rashin halartar tarukan da gwamnati ke gayyatarsa ba tare da bayar da wata kwakkwarar hujja ba. Hakan rashin biyayya ne.

A bayyane take cewa sau da dama Malam Muhammadu Sanusi II ya ki yin biyayya ga sashe na uku karamin kashe na 13 (a – e) na dokar Masarautar Kano State ta shekarar 2019 kuma idan aka bar shi ya ci gaba da haka, zai bata mutuncin Masarautar Kano.

Kare Mutuncin Kano

Sanarwar ta kara da cewa an dauki matakin tube wa Sarki Sanisu II rawaninsa ne domin kare mutunci da al’ada da addini da kuma kimar Masarautar Kano wacce aka gina shekaru dubbai da suka gabata.

Sukar Manufofin Gwamnati

Mai sharhi a kan harkokin siyasa, Kabiru Sa’idu Sufi, Malam a Kwalejin Share Fagen Shiga Jami’a da ke Kano, ya shiada wa BBC cewa babban dalilin cire Sarki Sanusi II daga kan mulki shi ne sukar da yake yi wa manufofin gwamnatin Gwamna Abdullahi Umar Ganduje. ya bayyana cewa sukar da ya yi wa shirin gwamnatin jihar na karbo bashi daga kasar China domin gina layin dogo a cikin birnin Kano.

A matsayinsa na masanin tattalin arziki, Sarkin na Kano ya ce babu wani alfanu da za a samu idan aka ciyo bashi domin aikin babu wata riba da Kano za ta samu da shi.

Wannan kalami ya fusata gwamnatin Kano, abin da ya sa aka fara takun-saka, kuma dangantaka ta fara yin tsami.

Lamarin ya kai ga yunkurin sauke Sarki daga sarauta da kuma kaddamar da bincike kan zargin kashe kudin masarauta ba bisa ka’ida ba.

Wasu manya da suka hada da mataimakin shugaban Kasa Yemi Osinbajo da Alhaji Aliko Dangote sun shiga tsakani domin sasanta gwamnan Kano da Sarkin Kano.

Sai dai Sarkin ya sha cewa an jujyawa maganganunsa.

Siyasa

Magoya bayan gwamnatin jihar Kano sun sha kokawa kan zargin da suke yi wa sarkin na shiga harkokin siyasa.

Gwamnan Kano da magoya bayansa sun zargi Sarki Sanusi da goyon bayan dan takarar jam’iyyar PDP a zaben gwamna.

Sun yi zargin cewa ya fito fili ya yaki Ganduje, kuma ya yi amfani da kudinsa wajen yi wa dan takarar gwamnan na jam’iyyar PDP yakin neman zabe, sai dai sarkin ya musanta wannan zargi.

Wannan dalili ne ya sa lokacin da Gwamna Ganduje ya ci zabe karo na biyu, magoya bayansa suka shiga wani babban dakin taro na gwamnatin jihar suka cire hoton Sarki Sanusi II.

Hakan ya janyo gagarumar baraka tsakanin shugabannin biyu, lamarin da ya kai ga gwamnatin na yunkurin tube sarkin.

Kirkirar karin masarautu hudu a cikin Masarautar Kano ya yi matyukar harzuka masarauta da kuma Sarkin Kano Muhammadu Sanusi II.

Masarautun da Gwamna Ganduje ya kirkira su ne: Gaya, Karaye, Bichi da kuma Rano.

Hakan ya sa masu nada sari a kano gurfanar da gwamnatin Ganduje a gaban kotu lamarin da ya sake rura rikicin da ke tsakanin Sarki Sanusi II da Gwamna Ganduje.

Previous Post

Ganduje Ya Sauke Sarkin Kano Muhammad Sunusi Na Biyu

Next Post

BREAKING: ASUU declares two-week warning strike

AB Gentle

AB Gentle

I Take Pictures Drink Chapman Eat And Sleep, CA Pro Graphics Designer, Cinematographer and A Blogger by Profession

Related Posts

University of Bath Global Leaders Scholarships in UK 2023/24

University of Bath Global Leaders Scholarships in UK 2023/24

by AB Gentle
June 1, 2023
0

...

Canada Visa: Express Entry Application 2023

Canada Visa: Express Entry Application 2023

by AB Gentle
June 1, 2023
0

...

McKinsey & Company Forward Learning Program 2023

McKinsey & Company Forward Learning Program 2023

by AB Gentle
June 1, 2023
0

...

German Bundestag IP Scholarship for Africans to Study in Germany

German Bundestag IP Scholarship for Africans to Study in Germany

by AB Gentle
June 1, 2023
0

...

Ashesi-ETH Masters in Engineering Scholarships 2023 [Fully Funded]

Ashesi-ETH Masters in Engineering Scholarships 2023 [Fully Funded]

by AB Gentle
June 1, 2023
0

...

Next Post

BREAKING: ASUU declares two-week warning strike

BREAKING: ABU Zaria Student Don't Go For Strike - See Why

Leave a Reply Cancel reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

SEARCH BAM

No Result
View All Result

ADVERTISMENT

HOT ENTRIES

University of Bath Global Leaders Scholarships in UK 2023/24

University of Bath Global Leaders Scholarships in UK 2023/24

June 1, 2023
Canada Visa: Express Entry Application 2023

Canada Visa: Express Entry Application 2023

June 1, 2023
McKinsey & Company Forward Learning Program 2023

McKinsey & Company Forward Learning Program 2023

June 1, 2023
German Bundestag IP Scholarship for Africans to Study in Germany

German Bundestag IP Scholarship for Africans to Study in Germany

June 1, 2023
Ashesi-ETH Masters in Engineering Scholarships 2023 [Fully Funded]

Ashesi-ETH Masters in Engineering Scholarships 2023 [Fully Funded]

June 1, 2023
  • About
  • Contact Us
  • Privacy Policy
  • DMCA/Disclaimer

Copyright © 2016 - 2023 BestArewaMusic Inc.

No Result
View All Result
  • Music
  • Videos
  • Hausa HipHop Music
  • News
  • International NEWS
  • Sports

Copyright © 2016 - 2023 BestArewaMusic Inc.